Ƴan ta’adda sun kai mummunan hari a Jihar Taraba

An kai Taraba wani mummunan hari a ƙauyen Ganfeto da ke Unguwar Daka na karamar hukumar Bali, ta jihar Taraba wanda ya kai ga rasa rayuka 10.

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, mutanen garin na cikin tashin hankali da kaduwa.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Taraba, Usman Abdullahi, ya tabbatar da wannan mummunan labari a cikin wata sanarwa da aka yi wa manema labarai a ranar Laraba a Jalingo, babban birnin jihar.

Ya bayyana cewa har yanzu ba a gano wadanda abin ya shafa ba.

Ya kuma nuna cewa ba a tabbatar da cewa maharan ‘yan fashi ba ne.

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Wasu ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karɓar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...