Ƴan Shi’a na zargin ƴan sanda da kashe mambobinsu huɗu a Kaduna

Ƙungiyar Yan’uwa Musulmi ta Najeriya wacce aka fi sani da shi’a  ta yi zargin cewa mambobin ta huɗu jami’an ƴan sanda suka kashe a Kaduna a ranar Juma’a.

Da yake magana da ƴan jaridu bayan yamutsin da ya faru, Aliyu Tirmizy ɗaya daga cikin jagororin ƙungiyar ya ce an kuma jikkata ƙarin wasu mutanen 20.

Tirmizy ya ce suna gudanar da zanga-zanga ne domin nuna goyon baya ga al’ummar Falasɗinawa amma sai ƴan sanda suka tarwatsa su.

“Yawanci muna fitowa a kowace Juma’a ta ƙarshen watan Azumin Ramadana domin yin zanga-zangar lumana ta nuna goyon baya ga Falasɗinawa kamar yadda ake a sauran  sassan duniya kan yadda ake musguna masu,” ya ce.

“Yawanci muna zanga-zangar cikin lumana amma a wannan karon muna shirin farawa sai ƴan sanda suka zo suka fara harba barkonon tsohuwa da kuma harbi inda suka kashe mambobin mu huɗu tare da jikkata wasu 20.”ya ce

Amma kuma mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jihar Kaduna,Mansir Hassan ya ce babu wanda aka kashe ya ƙara da cewa ba ayi amfani da harsashi ba wajen tarwatsa masu zanga-zangar.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani ɓangare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...