Ƴan sanda sun kama masu garkuwa da mutane da suka yi bacci a lokacin da suke tsare da mutanen da suka sace

Jami’an ƴan sanda sun samu nasarar kama wasu masu garkuwa da mutane bayan da suka buge da sharar bacci a lokacin da suke tsare da wasu mutane da suka sace.

An kama mutanen a yankin Ofosu dake jihar Ondo a lokacin da suka yi garkuwa da  matar wani fasto da kuma wasu mutane biyu.

Oladunlami  Ibukun mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar Ondo shi ne tabbatarwa da jaridar The Cable faruwar lamarin.

A cewar Ibukun mutanen da suka kuɓuta sun bayyana cewa sun tsere ne bayan da waɗanda suke tsare da su suka fara sharar bacci sakamakon ƙwayoyin maye  da suka sha.

“Mutanen ba a lokaci ɗaya suka kuɓuta ba,” a cewar mai magana da yawun rundunar.

Masu garkuwar da aka kama sun haɗa da Garba Mumini mai shekaru 27, Yusuf Tale shekaru 21, Kabiru Muhammad mau mai shekaru 16, Shaibu Umaru da Adamu Muhammad.

Ibukun ya ƙara da cewa masu garkuwar sun tsere daga jihar bayan da suka yi garkuwar a watan da ya wuce amma an kama musu bayan da ɗaya daga cikin mutanen da aka yi garkuwa da su ya gane ɗaya daga cikinsu.

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa ɗaya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faɗa tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...