Ƴan sanda sun kama mai garkuwa da mutane da ya kashe ɗan gidan ASP na ƴan sanda

Rundunar ƴan sandan jihar Bauchi ta kama wani mai suna, Rabi’u Adamu da ake zargi da yin garkuwa da kuma kisan wani yaro ɗan shekara 12 ɗan gidan ASP Bala Yarima.

A wata sanarwa ranar Juma’a, mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jihar,Ahmed Wakili ya ce wanda ake zargi mai shekaru 21 ya yi garkuwa tare da kashe Christopher Musa dake garin Magaman Gumau.

Wakili ya ce anyi garkuwa da marigayin ranar ranar 21 ga watan Maris lokacin da aka aike shi.

” A ranar 21 ga watan Maris 2024 da ƙarfe 08:00 na safe rundunar ƴan sandan jihar Bauchi ta samu kiran kai ɗaukin gaggawa na yin garkuwa da Christopher Bala ɗan gidan ASP Bala Yarima a garin Gumau,” a cewar sanarwar.

Biyo bayan binciken farko da aka yi wanda ake zargin ya amsa laifin shaƙe wuyan Christopher har ya mutu kuma ya amsa laifin  tatsar kuɗi har naira 200,000 daga mahaifin yaron.

Wanda ake zargin ya ce bayan da ya fuskanci cewa marigayin ya gane shi hakan ne ya sa ya kashe shi inda ya binne shi kusa da wani tsauni dake ƙauyen Bazale.

More News

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani ɓangare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...

Matatar Mai Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki A Ƙarshen 2024

Kamfanin Kaduna Refining and Petrochemical Company KPRC ya ce matatar mansa za ta fara aiki a shekarar 2024. Mustapha Sugungun managan matatar man ta KRPC...

Manyan dillalan mai za su fitar da litar man fetur miliyan 300 a wannan makon

Ƙungiyar MEMAN ta manyan dillalan man fetur da dangoginsa ta ce mambobinta sun fara lodin mai har lita miliyan 300 a cikin makon nan...

Kotu ta ɗaure mutumin sa ya yi sama-da-faɗi da kuɗin marayu

Babbar kotu a jihar Borno ta yanke wa Isiyaku Ibrahim hukuncin shekara ɗaya a gidan yari da zaɓin biyan tarar naira dubu 100 saboda...