Ƴan sanda a Kano sun kama wani ɗan daba da ya kashe wani matashi

Jami’an ƴan sanda a jihar Kano, sun samu nasarar kama wani ɗan daba da ya kashe wani matashi a unguwar Dorayi dake birnin Kano.

Matashin mai suna Abba Garba wanda aka fi sani da Ɗan Ƙuda dake zaune a unguwar Ɗorayi Chiranchi ana zarginsa da  kashe wani matashi mai suna, Zahraddeen Iliyasu ta hanyar caka masa wuƙa a wuya bayan da suka samu saɓani.

Kakakin rundunar ƴan sandan jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa shi ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar.

Ya ce an kama matashin ne lokacin da yake ƙoƙarin tserewa ya zuwa ƙasar Jamhuriyar Nijar.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani ɓangare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...

Matatar Mai Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki A Ƙarshen 2024

Kamfanin Kaduna Refining and Petrochemical Company KPRC ya ce matatar mansa za ta fara aiki a shekarar 2024. Mustapha Sugungun managan matatar man ta KRPC...