Ƴan Bindiga Sun Sako Ɗaliban Kuriga

Gwamnan jihar Kaduna,Mallam Uba Sani ya bayyana sakin ɗalibai 137 da aka yi garkuwa da su a garin Kuriga dake ƙaramar hukumar Chikun ta jihar Kaduna.

Gwamnan ya sanar da sakin ɗaliban ne cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Twitter da tsakar daren ranar Asabar.

“Ina sanar da cewa an sako  ɗaliban mu na makarantar Kuriga,”

Uba Sani ya godewa shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu kan yadda ya fifita tsaro da kare ƴan Najeriya musamman ta yadda ya tabbatar da cewa an sako ɗaliban makarantar.

A ranar 7 ga watan Maris ne wasu yan bindiga da ba’asan ko suwaye ba suka yi garkuwa da ɗaliban.

Gwamnan bai bayyana ko an biya kuɗin fansa ba kafin a sako ɗaliban.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...