Ƴan bindiga sun sace wasu matasa akan hanyarsu ta zuwa sansanin NYSC dake ‌Kebbi

Wasu yan bindiga a Zamfara sun yi garkuwa da wasu matasa da suka kammala jami’a akan hanyarsu ta zuwa sansanin yan yiwa kasa hidima dake jihar Kebbi.

Matasan sun fito ne daga jihar Akwa Ibom.

Eddy Megwa daraktan yaɗa labarai na hukumar ta NYSC dake Abuja shi ne ya tabbatar da faruwar lamarin.

Megwa ya ce anyi awon gaba da matasan ne da daddare a Zamfara lokacin da suke kan hanyarsu ta zuwa sansanin da aka tura su a jihar Kebbi.

Uku daga cikinsu sun samu nasarar tserewa a lokacin da yan bindigar suka tsare su.

Megwa ya kara da cewa yanzu haka shugaban hukumar ta NYSC yana Zamfara domin lalubo hanyar da za a kuɓutar da su.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani ɓangare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...