Yan bindiga sun kashe wani ɗan kasuwa, Alhaji Abdul Samiu Jimoh a garin Mokwa hedikwatar karamar hukumar Mokwa ta jihar Niger.
Lamarin ya faru ne da misalin karfe 08:00 na daren ranar Talata bayan da ya nuna turjiya a kokarin da yan bindigar suka yi na yin awon gaba da shi daga shagonsa.
Wani mazaunin garin ya fadawa jaridar Daily Trust cewa “An harbe ɗan kasuwar ne saboda yaƙi yarda ƴan bindigar su tafi da shi bayan da suka dage dole sai ya bi su. A lokacin da yake ja-inja da su ne suka harbe shi.”
Mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar Niger, DSP Wasiu Abiodun ya tabbatar da faruwar lamarin cikin wata sanarwa da ya fitar.
Sanarwar ta ce kafin jami’an yan sanda su isa wurin tuni yan bindigar sun tsere bayan sun harbe shi inda aka garzaya da shi babban asibitin Mokwa anan likitoci suka tabbatar da mutuwrsa.