Ƴan bindiga sun kashe wani ɗan kasuwa a jihar Neja

Yan bindiga sun kashe wani ɗan kasuwa, Alhaji Abdul Samiu Jimoh a garin Mokwa hedikwatar karamar hukumar Mokwa ta jihar Niger.

Lamarin ya faru ne da misalin karfe 08:00 na daren ranar Talata bayan da ya nuna turjiya a kokarin da yan bindigar suka yi na yin awon gaba da shi daga shagonsa.

Wani mazaunin garin ya fadawa jaridar Daily Trust cewa “An harbe ɗan kasuwar ne saboda yaƙi yarda ƴan bindigar su tafi da shi bayan da suka dage dole sai ya bi su. A lokacin da yake ja-inja da su ne suka harbe shi.”

Mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar Niger, DSP Wasiu Abiodun ya tabbatar da faruwar lamarin cikin wata sanarwa da ya fitar.

Sanarwar ta ce kafin jami’an yan sanda su isa wurin tuni yan bindigar sun tsere bayan sun harbe shi inda aka garzaya da shi babban asibitin Mokwa anan likitoci suka tabbatar da mutuwrsa.

More News

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...

An fara rushe wasu gine-gine 500 a kasuwar Karmo dake Abuja

Hukumar FCTA dake kula da birnin tarayya Abuja ta fara rushe gine-gine sama da 500 da aka yi ba bisa ka'ida ba a kasuwar...

Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa

A ranar Alhamis ne shugaba Bola Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa, a ziyarar da Faye ya...

NEMA ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo dasu gida daga ƙasar Chad

Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Ƙasa NEMA ta ce ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo da su bayan da su ka maƙale...