Gwamnatin Jihar Zamfara ta fara rabon buhunan taki 72,000 da sauran kayayyakin noma ga manoma domin ƙarfafa noman damina na shekarar 2026.
Gwamna Dauda Lawal ne ya ƙaddamar da shirin a Gusau. Ya ce gwamnati na son bunƙasa harkar noma, ƙara yawan abinci da inganta tattalin arzikin jihar.
Shirin ya haɗa da rabon taki, magungunan kashe ciyawa, injunan aikin gona, iri masu inganci da sauran kayan tallafawa manoma.
Gwamnan ya kuma bayyana cewa za a raba kayayyakin ga dukkan gundumomi 147 da ke ƙananan hukumomi 14 na jihar, domin tabbatar da cewa manoma sun samu tallafin da zai ƙara yawan amfanin gonarsu.
Zamfara Ta Fara Raba Buhunan Taki 72,000 Ga Manoma

