Zamfara: Shin kashe-kashen gilla karuwa yake a Najeriya?

[ad_1]

A woman in the Nigerian special forces

Hakkin mallakar hoto
Getty Image


Rundunar sojin kasar ta kai dakaru don shawo kan lamarin

Ana ci gaba da damuwa a Arewacin Najeriya kan yawan hare-hare da kuma satar mutane da ake yi a jahar Zamfara.

A cikin wani bidiyon da aka wallafa a baya-bayan nan, wata ‘yar jarida a kasar Kadaria Ahmed ta soki gwamnati kan ikrarinta na cewa ana ta samun karuwar kashe-kashe a yankin.

”A kullum dai muna binne a kalla mutum 30 ko 40 ko kuma 50,” kamar yadda ta fadi hakan a wani bidiyo, da kuma a wani jawabin da ta gabatar a talbijan wanda aka kuma yada sosai a shafukan sada zumunta.

Ta ce ana kashe mutane a Zamfara fiye da yadda ake kashe mutane a Borno da Adamawa da kuma Yobe, jihohi kenan a yankin arewa maso gabashin Najeriya wadanda ‘yan kungiyar Boko Haram su ke yawan kai hare-hare.

To me ke faruwa a Zamfara, kuma yawan tashin hankali na karuwa ne a jihar?

Zamfara dama ta dade tana fama da matsalar sace-sacen dabobi, da dauke mutane domin samun kudin fansa da kuma kai hare-hare kan al’ummomi, wanda hakan ya tilasta wa wasu mazauna yankin suka hada kai wajen samar da kungigoyin ‘yan banga.

A ‘yan kwannakin nan dai, an samu karuwar hakar ma’adinai ba ta halattacciyar hanya ba a yankin mai dumbin arzikin ma’adinai, hakan ya janyo shigowar baki da dama, daya daga cikin abubuwan da ke kara hana zaman lafiya a yankin kenan.

A farkon watan Afrilun 2019, gwamnati ta mayar da martani kan damuwar karin hare-haren da a ke kaiwa, ta kuma dakatar da dukkanin ayyukan hakar ma’adinai a jahar, tare da aika dakarun tsaro zuwa yankin.

Wata cibiyar kula da yawan tashe-tashen hankula a Najeriya – The Nigeria Security Tracker, wanda hukumar kula da harkokin kasashen waje a birnin Washington (CFR) ta kafa, tana kula da yawan tashe-tashen hankula ta hanyar bincike kan rahotannin da kafafen yada labarai a kasar ke wallafawa.

Wannan na nuna cewa an samun karuwar kashe-kashe a cikin ‘yan makkonin da suka gabata.

A cewar wadanan nambobin, tun farkon 2019, an samu mutuwar fararen hula 262. A cikin 2018 gaba daya an samu 288, a 2017 kuma 52.

Hasashen na CFR ya nuna karuwar kashe ‘yan kungiyar bindiga – a ciki har da ‘yan ta’adda da ‘yan banga da kuma duk wanda ya ke da hannu a harkokin rashin gaskiya.

Amma, yawan mutanen da ke mutuwa a kowace rana bai kai 30 da 50 inda Kadaria Ahmed ta bayyana cewa ana samu ba.

Fararen hula 262 ne suka mutu a cikin kwana 100 na wannan shekarar, hakan na nufin kenan mutum biyu ko uku ne ke rasa rayyukansu a kowace rana, duk da yawan da CFR ta fitar ba ta bayyana cewa yawan wadanda ke rasa rayukansu na karuwa ba.

Kwatanta Zamfara da sauran jihohin Arewacin Najeriya

A cikin bidiyonta, Kadaria Ahmed ta kuma yi zargin cewa an fi samun tashe-tashen hankula a Zamfara fiye da yadda ake samu a jihohin da ke yankin arewa maso gabashin kasar, inda ‘yan Boko Haram su ke yawan kai hare-hare.

Idan aka dauki dukkanin mace-macen fararen hula da aka samu tun farkon watan Maris har zuwa shida ga watan Afrilu, an samu mutuwar mutum 169 a Zamfara a cewar CFR – an kwatanta wannan da mutum 28 da suka mutu a Borno da kuma 14 a Adamawa.

Ba a samu irin lamarin a Yobe ba.

Saboda haka hasashen Kadaria Ahmed daidai yake, inda ta ce an fi samun mace-macen mutane a Zamfara idan aka kwatanta su da wadancan sauran jihohin.

Raguwar yawan kashe-kashen da ake yi a Borno da Adamawa da kuma Yobe na faruwa ne sakamakon yawan kwace yankunan da ke karkashin ikon ‘yan Boko Haram da ake yi tun a shekara ta 2015.


Karin bayani game da Zamfara:

  • Kashi 67.5 na mutanen jihar na cikin talauci (kashi 62 kenan cikin 100 na masu fama da talauci a kasar)
  • Yawan mutanen da ke fama da rashin ilimi: kashi 54.7 cikin 100
  • Taken jihar: Noma shi ne abin da muke alfahari da shi
  • Mazauna jihar yawanci manoma ne daga al’ummomin Hausawa da kuma Fulani
  • Yawan al’umma : Miliyan 4.5 ( hasashen da aka yi a 2016)
  • Ma fi yawan al’ummar jihar Musulmai ne
  • Ita ce jiha ta farko da ta kaddamar da shari’ar Musuluncia shekarar 2000

More News

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...

An kori sojojin Najeriya biyu saboda satar kebul a matatar Dangote

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da korar wasu sojoji biyu da ake zargi da satar igiyoyin sulke a harabar matatar Dangote da ke jihar...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...