Zaman fursuna na shekara 3 ko tarar $3,000 ga masu shan shisha

shisha

Wuraren da ake shan tabar shisha a Ghana za su dinga fuskantar hukunci mai tsanani idan har ba su bi dokokin kiyaye lafiya da kasar ta tanadar ba.

Shan tabar Shisha dai ya zama ruwan dare a tsakanin matasa a kasar.

Sai dai akwai sabanin ra’ayi kan cewa tabar shisha ba ta da illa kamar taba sigari.

Amma Hukumar Lafiya Ta Duniya WHO da Hukumar Kula da Abinci da Magunguna ta Ghana FDA, ba su yarda da wannan batu ba.

Hukumar ta ce daga yanzu duk mai mashayar da aka kama ana shan shisha a wajen zai fuskanci zaman gidan yari na shekara uku ko a ci shi tarar dala dubu uku, kwatankwacin naira miliyan daya da 80,000 kenan.

Sai dai wannan hukunci zai hau kansu ne kawai idan ba su yi rijistar shishar ba ko kuma idan ba su sanya sanarwar gargadi kan irin hadarin da ke tattare da shanta yake ba.

Yayin shan shisha

Shan wannan taba mai kanshin gaske na kara karbuwa a wurin jama’a a fadin duniya, amma masana harkar lafiya sun ce mafi yawan wadanda suke shanta ba su san hadarin da ke tattare da hakan ba.

Yanzu dai mutane ne da dama suke cin moriyar wannan taba wadda ke tashe a Indiya da Gabas ta tsakiya inda aka ce daga nan ta samo asali.

A Gabas ta tsakiya yayin ya ratsa har tsakanin ‘yan yara maza da mata da ma manyan mata wadanda yawancinsu ba sa shan taba.

Wannan yayi yanzu ya kai har ga kasashen Turai da Brazil da kuma Amurka inda za ka ga shagunan shan wannan taba mai zamani.

Shugaban sashen tiyatar zuciya a babban asibitin kasa na Saudi Arabia, National Guard Health Affairs, Farfesa Hani Najm, ya taba sheda wa BBC a wata tattaunawa cewa yana fargaba shan tabar shisha zai iya kara yawan masu cutukan zuciya a kasashen yankin Gabas ta tsakiya.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...