Za mu sake duba shirin tallafin N8000 ga ƴan Najeriya

A wani al’amari na baya-bayan nan, Shugaba Bola Tinubu ya bayyana sake fasalin shirin farko na raba tallafin kudi na Naira 8,000 ga gidaje miliyan 12 duk wata na tsawon watanni shida.

Matakin dai ya zo ne a matsayin mayar da martani ga sukar jama’a da damuwar da kungiyoyin kwadago suka yi, wadanda ke ganin cewa shirin ya gaza wajen rage wahalhalun da ke tattare da cire tallafin man fetur.

Da yammacin ranar Talata, wata sanarwa da Dele Alake, mai baiwa shugaban kasa shawara kan ayyuka na musamman, sadarwa, da dabaru ya fitar, ta mika umarnin shugaban kasa na sake duba shirin mika kudi naira 8,000 da aka kayyade da nufin samar da agaji ga gidaje masu rauni.

Tinubu ya ba da umarnin cewa a gaggauta bayyana dukkanin matakan da gwamnati ta dauka na rage wa al’ummar Najeriya wahala.

More from this stream

Recomended