Yawan mutanen da suka mutu a hatsarin motar shanu a Kano ya karu zuwa 23

Hukumar kula da kiyaye afkuwar hatsura ta ƙasa FRSC shiyar jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu a hatsarin motar da ya faru a jihar ya karu zuwa mutane 23.

A ranar Juma’a ne wata motar tirela dake ɗauke da dabbobi  da mutane ta ƙwace ta faɗi a  gadar sama ta Muhammadu Buhari dake kan titin Maiduguri a birnin.

A wata sanarwa ranar Juma’a, Abdullahi Labaran mai magana da yawun hukumar a jihar ya ce mutane 48 ne suka jikkata a hatsarin.

Labaran ya ce tukin ganganci da direban yake yi shi ne ya jawo motar ta ƙwace ta faɗi abin da ya haifar da asarar rayuka da dukiya.

Jumillar mutane 71 ne hatsarin ya rutsa da su a  cewar sanarwar da hukumar ta fitar.

More from this stream

Recomended

Mutane 7 Sun Rasa Rqyukansu, 53 Sun Jikkata Sakamakon Guguwar Iska a Jigawa

Akalla mutane bakwai sun rasa rayukansu, yayin da 53 suka jikkata bayan wata guguwar iska ta yi barna a kananan hukumomi 13 na jihar Jigawa. Rahotanni sun nuna cewa guguwar ta shafi gidaje 5,403 a cikin garuruwa 120, inda ta lalata makarantu sama da 47, asibitoci uku, ofisoshin ‘yan sanda biyu, gidajen zama da sauran […]