Yaro dan shekara 7 ya fada rijiya ya mutu – AREWA News

Hukumar kashe gobara ta jihar Kano,ta ce wani yaro mai shekaru 7 ya mutu bayan da ya fada rijiya a layin Yarabawa dake Unguwa Uku a karamar hukumar Tarauni dake jihar.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar, Sa’idu Muhammad ya fitar a ranar Laraba.

Muhammad ya ce lamarin ya faru ne da yammacin ranar Talata lokacin da yaron yaje ɗibar ruwa.

“Mun samu kiran kai ɗaukin gaggawa daga Abdularauf Abba da misalin karfe 06:00 na yamma da samun labarin munyi gaggawar tura jami’an mu na aikin ceto inda suka isa da karfe 06:07.”

“An ciro gawar yaron daga cikin rijiyar aka kai ta asibitin kwararru na Murtala Muhammad inda aka tabbatar da mutuwarsa,” ya fadawa kamfanin dillancin labarai na NAN.

More from this stream

Recomended

Mutane 7 Sun Rasa Rqyukansu, 53 Sun Jikkata Sakamakon Guguwar Iska a Jigawa

Akalla mutane bakwai sun rasa rayukansu, yayin da 53 suka jikkata bayan wata guguwar iska ta yi barna a kananan hukumomi 13 na jihar Jigawa. Rahotanni sun nuna cewa guguwar ta shafi gidaje 5,403 a cikin garuruwa 120, inda ta lalata makarantu sama da 47, asibitoci uku, ofisoshin ‘yan sanda biyu, gidajen zama da sauran […]