Yaro dan shekara 7 ya fada rijiya ya mutu – AREWA News

Hukumar kashe gobara ta jihar Kano,ta ce wani yaro mai shekaru 7 ya mutu bayan da ya fada rijiya a layin Yarabawa dake Unguwa Uku a karamar hukumar Tarauni dake jihar.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar, Sa’idu Muhammad ya fitar a ranar Laraba.

Muhammad ya ce lamarin ya faru ne da yammacin ranar Talata lokacin da yaron yaje ɗibar ruwa.

“Mun samu kiran kai ɗaukin gaggawa daga Abdularauf Abba da misalin karfe 06:00 na yamma da samun labarin munyi gaggawar tura jami’an mu na aikin ceto inda suka isa da karfe 06:07.”

“An ciro gawar yaron daga cikin rijiyar aka kai ta asibitin kwararru na Murtala Muhammad inda aka tabbatar da mutuwarsa,” ya fadawa kamfanin dillancin labarai na NAN.

More News

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...