
Rundunar ‘yan sandan jihar Kebbi ta sanar da tsare wasu jami’anta uku bisa zarginsu da hannu a kisan wani da ake zargi da sata a garin Jega.
Mai magana da yawun rundunar, CSP Nafi’u Abubakar, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar a Birnin Kebbi.
A cewar sanarwar, lamarin ya samo asali ne daga rahoton satar tayoyin babbar mota da wani ya kai ofishin ‘yan sanda na Division a Jega.
CSP Abubakar ya jaddada cewa rundunar tana jajirce wajen tabbatar da bin ka’idoji da dabi’un aikin dan sanda.