Yan sanda sun kama mutane uku da ke shirin sace daliban sakandare a Kebbi – AREWA News

Rundunar yan sandan jihar Kebbi ta kama wasu mutane uku da ake zargi da shirya yin garkuwa da daliban makarantar sakandaren fasaha ta gwamnatin tarayya dake Zuru.

Yayin da yakewa yan jaridu jawabi kwamishinan yan sandan jihar, Garba Danjuma ya ce mutane ukun da ake zargi da shirin yin garkuwa da daliban sun fito ne daga jihar Kebbi.

Ya ce tunda fari sun rubutawa shugaban makarantar wasika kan shirinsu na kai hari makarantar tare da sace dukkanin dalibanta.

Kwamishinan ya ce wani mai suna,Sani Shehu da kuma dansa, Muhammad A. sani daga jihar Yobe sune aka kama kan shirya harin.

More from this stream

Recomended

Mutane 7 Sun Rasa Rqyukansu, 53 Sun Jikkata Sakamakon Guguwar Iska a Jigawa

Akalla mutane bakwai sun rasa rayukansu, yayin da 53 suka jikkata bayan wata guguwar iska ta yi barna a kananan hukumomi 13 na jihar Jigawa. Rahotanni sun nuna cewa guguwar ta shafi gidaje 5,403 a cikin garuruwa 120, inda ta lalata makarantu sama da 47, asibitoci uku, ofisoshin ‘yan sanda biyu, gidajen zama da sauran […]