Rundunar yan sandan jihar Kebbi ta kama wasu mutane uku da ake zargi da shirya yin garkuwa da daliban makarantar sakandaren fasaha ta gwamnatin tarayya dake Zuru.
Yayin da yakewa yan jaridu jawabi kwamishinan yan sandan jihar, Garba Danjuma ya ce mutane ukun da ake zargi da shirin yin garkuwa da daliban sun fito ne daga jihar Kebbi.
Ya ce tunda fari sun rubutawa shugaban makarantar wasika kan shirinsu na kai hari makarantar tare da sace dukkanin dalibanta.
Kwamishinan ya ce wani mai suna,Sani Shehu da kuma dansa, Muhammad A. sani daga jihar Yobe sune aka kama kan shirya harin.