Sojoji Sun Kama Wasu Jami’asu Guda Biyu Kan Zargin Cin Zarafin Farar Hula a Filato


Dakarun Operation Enduring Peace sun kama wasu sojoji biyu bisa zargin hannu a wani rikici da ya jikkata ’yan sintiri uku da wata mata a ƙaramar hukumar Jos ta Kudu a jihar Filato.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne a yankin Kugiya da ke Bukuru bayan wata saɓani da ya shafi ƙwace babur da kuma zargin kasancewar wasu masu ɗauke da makamai a wurin.

Majiyoyin tsaro sun bayyana cewa dakarun Sector 6 na Operation Safe Haven sun isa wurin bayan samun kiran gaggawa, inda suka tarar da wasu ’yan sintiri uku da wata mata mai suna Mrs. Kaneng Nyang Bot da raunuka.

An bayyana sunayen sojojin da aka kama da Pte. Adam Saheed da Gnr. Mohammed Shuaibu. Rahotanni sun ce ana ci gaba da tsare su domin fuskantar matakan ladabtarwa da bincike.

More from this stream

Recomended

Mutane 7 Sun Rasa Rqyukansu, 53 Sun Jikkata Sakamakon Guguwar Iska a Jigawa

Akalla mutane bakwai sun rasa rayukansu, yayin da 53 suka jikkata bayan wata guguwar iska ta yi barna a kananan hukumomi 13 na jihar Jigawa. Rahotanni sun nuna cewa guguwar ta shafi gidaje 5,403 a cikin garuruwa 120, inda ta lalata makarantu sama da 47, asibitoci uku, ofisoshin ‘yan sanda biyu, gidajen zama da sauran […]