‘Yan Bindigar Zamfara Sun Kashe Mutane 13

A wani al’amari mai daure kai, wasu mahara, wadanda wasu ke zargin cewa ‘yan yankin ne, sun sake kai hari a kauyen Gidan Kaso da ke Karamar Hukuma Birnin Magaji ta jahar Zamfara, inda su ka kashe mutane akalla 13 baya ga wadanda su ka ji ma raunuka da kuma dukiyar da au su ka sace au su ka barnata.

Wasu ganau kuma mazauna kauyen na Gidan Kaso, wadanda su ka bukaci a sakaya sunayensu saboda tsoron abin da ka biyo baya, sun ce maharan sun isa garin ne da babura kuma sabe da bindigogi da yammacin jiya Asabar su ka shiga bude wuta da kuma kone-kone. Su ka ce kusan duk wayewar gari sai wadannan maharan sun far ma wasu mutane a yankin. Su ka ce saboda yawan kai hare-haren da mutanen ke yi, har manoman yankin sun kasa zuwa gonakinsu duk kuwa da damina ta kankama.

‘Yan yankin su ka ce idan ma an girke sojoji a Birnin Magaji, kamar yadda hukumomi ke ikirari, to girke sun bai yi wani tasiri ba – a kalla ya zuwa yanzu dai. Haka ma jiragen sintirin da ke tauna tsakuwa a yankin; sun ce bas u hana miyagun cin karansu ba babbaka.

Duk wani kokari na jin ta bakin ‘yan sanda ya ci tura.

More News

Ɗalibai a Jami’ar Jos na zanga-zanga saboda rashin wuta da ruwa

Wasu daliban jami’ar Jos da ke jihar Filato a ranar Alhamis sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matsalar karancin ruwa da rashin...

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...