
Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya tabbatar wa ’yan Najeriya cewa gwamnatinsa za ta kawo ƙarshen matsalar ta’addanci da ’yan bindiga a faɗin ƙasar.
A saƙonsa na Babbar Sallah da ya fitar ranar Talata, Tinubu ya amince cewa hare-haren da ya kira na “’yan ta’adda da ’yan bindiga marasa tausayi” na ci gaba a wasu al’umma. Sai dai ya ce gwamnati ba ta yi watsi da waɗanda matsalar tsaro ta shafa ba.
Ya ce, “Za mu murƙushe dukkan miyagun ƙarfi a ƙarshe.”
Shugaban ya kuma kare manufofin tattalin arzikin gwamnatinsa, inda ya ce sauye-sauyen da aka aiwatar cikin shekaru uku da suka gabata sun fara haifar da sakamako mai kyau.
A cewarsa, “Tafiyar cikin duhun rami ta ƙare, yanzu haske ya bayyana.”
Tinubu ya ce an samu ci gaba a yaƙi da rashin tsaro, ciki har da kashe wani shugaban ISIS da hukumomi ke nema ruwa a jallo. Ya ƙara da cewa gyare-gyaren da ake yi a ɓangaren tsaro za su taimaka wajen samar da zaman lafiya da ƙarin damar tattalin arziki.
Haka kuma ya bayyana Babbar Sallah a matsayin lokaci na tunawa da muhimmancin imani, sadaukarwa, tausayi da haɗin kai, tare da kira ga Musulmi da su yi addu’ar zaman lafiya da haɗin kan ƙasa.