Yan bindiga sun kashe wani ma’aikacin kiwon lafiya a Zamfara

Yan bindiga sun kashe, Mallam Lawali Musa wani ma’aikacin lafiya a wani hari da suka kai da daddare a garin Moriki dake karamar hukumar Zurmi ta jihar Zamfara ranar Talata.

Yan bindiga sun kuma samu nasarar yin garkuwa da mutane 8 daga garin a harin da suka kai wanda ya ɗauki tsawon minti kamar yadda wasu mazauna garin suka faɗawa jaridar 21 Century Chronicles.

A cewar majiyar  an kashe Lawal ne bayan da yaki yarda yan bindigar su yi garkuwa da shi lokacin da suka shiga gidansa.

“Sun so  daukarshi zuwa cikin daji amma ya ce ba zai bi su ba abun da ya jawo yan bindigar su ka har be shi,” a cewar wani abokin aikinsa a hirar da ya yi jaridar 21 Century Chronicles.

Huɗu daga cikin mutane uku da aka yi garkuwa da su ƴaƴan marigayin ne.

Kawo yanzu rundunar yan sandan jihar Zamfara bata fitar da wata sanarwa ba kan harin.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]