Yan bindiga sun kashe wani jigon jam’iyar PDP a jihar Osun

Yan bindiga sun kashe, Richard Idowu wani jigo a jam’iyar PDP ta jihar Osun kuma mai neman tsayawa takarar kujerar É—an majalisar tarayya a karkashin jam’iyar.

Richard wanda aka fi sani da Ade Ori Okin an harbe shi har lahira a cikin wani gini da ba a kammala ba dake wajen garin Ejigbo inda marigayin ya gudanar da wani taron siyasa da yan siyasa da kuma mutanen Ejigbo da yammacin ranar Asabar.

Har ila yau an harbe wani mutum na daban a wani daji dake kusa da gidan da aka harbe É—an sisayar.

Gwamnan jihar, Ademola Adeleke ya umarci kwamishinan yan sandan jihar da gudanar da bincike domin zaƙulo waɗanda suke da hannu kan faruwar lamarin.

Kwamishinan ƴada labarai na jihar, Oluomo Kolapo Alimi ya roƙi mazauna jihar da su kwantar da hankali inda ya tabbatar musu cewa za a binciki lamarin tare da hukunta wanda suka aikata laifin.

Kawo yanzu dai an kama mutum guda wanda ake zargin yana da hannu a kisan kan.

More News

Manyan dillalan mai za su fitar da litar man fetur miliyan 300 a wannan makon

Ƙungiyar MEMAN ta manyan dillalan man fetur da dangoginsa ta ce mambobinta sun fara lodin mai har lita miliyan 300 a cikin makon nan...

Kotu ta É—aure mutumin sa ya yi sama-da-faÉ—i da kuÉ—in marayu

Babbar kotu a jihar Borno ta yanke wa Isiyaku Ibrahim hukuncin shekara ɗaya a gidan yari da zaɓin biyan tarar naira dubu 100 saboda...

NFF ta naÉ—a Finidi George a matsayin sabon kocin Super Eagle

An naɗa Finidi George a matsayin sabon mai horar da kungiyar ƙwallon ƙafar Najeriya wato Super Eagle. Hukumar ƙwallon Ƙafa ta Najeriya, NFF ita ta...

Gwamnan Edo Zai Fara Biyan 70,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

Gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki ya sanar da mafi ƙarancin albashi ga ma'aikatan ga ma'aikatan jihar inda za a riƙa biyan naira dubu 70,000. Gwamnan...