Yan bindiga sun kashe mutane uku a Katsina – AREWA News

Mutane uku aka rawaito an kashe tare da jikkata wasu uku a wani hari da yan bindiga suka kai kan kauyen Marar Zamfarawa dake karamar hukumar Dan Musa a jihar Katsina.

Yan bindigar da suka isa kauyen da kafa sun kaddamar da harin ne da tsakar daren ranar Juma’a.

Mazauna kauyen da kuma jami’an tsaro sun fuskanci su a kokarin da su kayi na dakile harin.

A cewar mazauna kauyen waɗanda aka kashe sun hada da Aminu Yusuf, Lawal Akushi da Mansir Danliti wadanda kuma suka jikkata sun hada da Rabi’u Mala, Shamsu da kuma Sharhabilu da ake yi musu magani a babban asibitin Danmusa.

An binne wadanda suka mutu ranar Asabar da safe bayane da aka yi musu jana’iza.

More News

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...