Yan bindiga sun kashe mutane uku a Katsina – AREWA News

Mutane uku aka rawaito an kashe tare da jikkata wasu uku a wani hari da yan bindiga suka kai kan kauyen Marar Zamfarawa dake karamar hukumar Dan Musa a jihar Katsina.

Yan bindigar da suka isa kauyen da kafa sun kaddamar da harin ne da tsakar daren ranar Juma’a.

Mazauna kauyen da kuma jami’an tsaro sun fuskanci su a kokarin da su kayi na dakile harin.

A cewar mazauna kauyen waɗanda aka kashe sun hada da Aminu Yusuf, Lawal Akushi da Mansir Danliti wadanda kuma suka jikkata sun hada da Rabi’u Mala, Shamsu da kuma Sharhabilu da ake yi musu magani a babban asibitin Danmusa.

An binne wadanda suka mutu ranar Asabar da safe bayane da aka yi musu jana’iza.

More from this stream

Recomended

Mutane 7 Sun Rasa Rqyukansu, 53 Sun Jikkata Sakamakon Guguwar Iska a Jigawa

Akalla mutane bakwai sun rasa rayukansu, yayin da 53 suka jikkata bayan wata guguwar iska ta yi barna a kananan hukumomi 13 na jihar Jigawa. Rahotanni sun nuna cewa guguwar ta shafi gidaje 5,403 a cikin garuruwa 120, inda ta lalata makarantu sama da 47, asibitoci uku, ofisoshin ‘yan sanda biyu, gidajen zama da sauran […]