Yadda mahara suka kashe ma’aikaciyar Aso Rock

Fadar Shugaba Buhari

Fadar shugaban Najeriya ta bayyana alhininta kan kisan da aka yi wa Ms Laetitia Naankang Dagan, wadda mataimakiyar darakta a bangaren mulki ce a Fadar Shugaban kasa.

Alhinin na kunshe cikin wata sanarwa da Attah Isa, mataimakin shugaban sashin hulda da jama’a ya sanya wa hannu.

A sanarwar, babban sakatare a Fadar Shugaban Najeriyar da ke Abuja, Jalal Arabi ya bayyana kisan da aka yi wa Ms Leticia a matsayin babban rashi ga iyalanta har ma ga daukacin ma’aikatan Fadar Shugabn Kasa.

“Ma’aikaciya ce mai sadaukar da kai kuma mai aiki tukuru, kuma mun ji zafin kisan gillar da aka yi ma ta:, inji Arabi yayin wata ziyara da ya kai ga ‘yan uwan mamaciyar.

Arabi ya kuma bayyana karfin gwuiwa cewa ‘yan sanda za su gano wadanda ke da alhakin kisan Ms Leticia, kuma doka za ta yi halinta a kansu.

Ms Dagan mai shekara 47 ‘yar asalin jihar Filato ce. Ta yi aiki har kimanin karfe 8 na daren Litinin a ofishinta.

Amma da misalin karfe 11 na daren sai wasu wadanda ba a san ko suwa ne ne ba suka kashe ta a cikin gidanta.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...