Yaƙin Sudan: Mutane sama da 7,000, ciki har da ƴan Najeriya, sun tsangare a Misra

Gwamnatin tarayya a ranar Juma’a ta yi kira ga hukumomin da abin ya shafa a kan iyakokin kasar Sudan da su samar da yanayin jin dadin jama’a ga ‘yan kasar kimanin 7,000 ciki har da ‘yan Najeriya, su samu damar shiga wurare daban-daban ba tare da wata matsala ba.

Shugabar hukumar ‘yan Najeriya mazauna kasashen waje, Abike Dabiri-Erewa, wacce ta yi wannan kiran, ta ce ba a ba ‘yan kasar damar tsallakawa kasar Masar ba tun zuwansu da yammacin ranar Alhamis.

Dabiri-Erewa, a ranar Alhamis, ta tabbatar da isowar rukunin farko na ‘yan Najeriya da suka makale a Sudan a kan iyakar Aswan a Masar.

Dabiri-Erewa, wadda ta tabbatar da faruwar lamarin a wani sako da ta wallafa a shafinta na Twitter, ta ce tuni aka rufe kan iyakar lokacin da daliban suka isa wurin.

Sai dai a wata sanarwa mai dauke da sa hannun Gabriel Odu, Sashen Watsa Labarai na NiDCOM, ya ce “Tawagar Najeriya a Masar ta yi aiki tukuru a kan hakan yayin da mahukuntan Masar ke nanata bayar da biza ta ‘yan kasashen Afirka don komawa kasashensu.

“Ta yi kira ga hukumomin Masar da su ba wa matafiya da suka kaɗu damar wucewa zuwa kasashensu daban-daban na Afirka.”

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani ɓangare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...