Wata matashiya ‘yar shekara 28 ta maka surukarta a kotu saboda ta kira ta da sunan “karuwa” a garin Rigasa cikin jihar Kaduna da ke arewacin Najeriya.
Kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN ya ambato Hadiza Safiyanu tana shaida wa kotun Shari’ar Musulunci cewa ita da mijinta suna zaune ne a gida daya da uwar mijinta tun bayan aurensu.
Ta ce: “Wata rana da misalin karfe 11 na dare surukar ta shigo dakina ta fara kira na da karuwa, ta kuma ce min in bar mata gidanta saboda mijina ya sake ni.
“Ni kuma na ki tafiya saboda lokacin dare ya yi. Sai ta dauko sanda ta fara dukana, ta kuma kira ni da wasu sunayen da ba za su fadu ba.
Hadiza ta ce tun daga wannan lokaci ne ta fice daga gidan, inda yanzu take zaune a gidan kakanta.
Ta ce tana bukatar kotun ta tabbatar mata da sakin sannan ta debo sauran kayanta daga gidan.
Wadda ake zargin Aisha Lamido ta musanta zarge-zargen da ake mata.
Mai shari’a Dahiru Lawal ya bai wa Hadiza umarnin ta gabatar da shaidunta a ranar 20 ga watan Yuni.