Wani ya harbe mutum 5 saboda sun dame shi da surutu

Rasha

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

—BBC Hausa

Wani mutum a kasar Rasha ya harbe mutum biyar saboda sun dame shi da surutu a kofar gidansa da dare.

‘Yan sanda sun ce lamarin ya faru ne a kauyen Yelatma da ke yankin Ryazan mai nisan kilomita 200 daga kudu maso gabashin birnin Moscow.

Yankin yana killace saboda annobar coronavirus da ake fama da ita.

Bincike ya nuna cewa mutumin ya gargadi mutanen daga barandar benensa. Nan take hayaniya ta barke tsakaninsu kuma ya bude musu wuta da wata bindigar farauta.

Maza hudu da mace daya sun mutu nan take sakamakon raunin da suka ji da karfe 10:00 na daren Asabar, a cewar kwamitin da ke binciken lamarin.

An kama wanda ake zagin da ba a bayyana sunansa ba. An bincika gidansa kuma aka kwace bindigar tasa.

More News

ÆŠalibai a Jami’ar Jos na zanga-zanga saboda rashin wuta da ruwa

Wasu daliban jami’ar Jos da ke jihar Filato a ranar Alhamis sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matsalar karancin ruwa da rashin...

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...