Tinubu zai tafi kasar Turkiyya ranar Litinin

A ranar Litinin ake sa ran shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu zai tafi ƙasar Turkiyya a wata ziyarar aiki da zai kai kasar.

A wata sanarwa  da aka fitar ranar Lahadi, mai magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga ya ce Tinubu zai kai ziyarar ne domin sake karfafa alakar dake akwai  tsakanin ƙasashen biyu da kuma sake lalubo wasu fannoni na haɗin kai a bangaren sufurin jiragen sama, tsaro, cigaban al’umma da kuma kirkire-kirkire.

Onanuga ya ce fannin kuɗi, sadarwa, kasuwanci da kuma zuba jari su ne za su kasance a gaba-gaba akan batutuwan da za a tattauna a tsakanin ƙasashen biyu.

Ya kara da cewa Najeriya da Turkiyya za su rattaba hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna kan ɓangaren binciken kimiyya, fasahar makamashi da kauna fannin tsaro.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]