Tinubu ya tura tawagar manyan jami’an gwamnati garin Ogbomoso inda aka sace dalibai

A ranar Lahadi tawagar shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu a ƙarƙashin jagorancin shugaban ma’aikatan fadar shugaban ƙasa, Femi Gbajabiamila  ta isa garin Ogbomoso dake jihar Oyo biyo  bayan da aka yi garkuwa da Malamai da kuma ɗalibai daga wasu makarantu dake karamar hukumar Oriire ta jihar.

An yi garkuwa da mutanen ne a ranar 15 ga watan Mayu daga wasu makarantun sakandare na firamare bayan da wasu yan bindiga su ka kai farmaki makarantun.

Aƙalla ɗalibai da malamai 45 ne yan bindiga su ka yi awon gaba da su.

Tawagar da ta isa garin Ogbomoso a cikin wani jirgi mai saukar ungulu na dauke da mai bawa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu, Babban Sifetan Yan sandan Najeriya, Tunji Disu da kuma ministan tsaro, Christopher Musa mai ritaya.

A yayin ziyarar tawagar ta gana da iyalan mutanen da abin ya shafa da kuma shugabannin al’umma.

More from this stream

Recomended