Tinubu ya tafi ƙasar Faransa

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu zai tafi ƙasar Faransa a ranar Laraba a wata ziyara da zai kai ta ƙashin kansa.

A wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasar, Bayo Onanuga ya fitar ta ce Tinubu zai gana da shugaban kasar,Faransa Emmanuel Macron a yayin ziyarar.

Onanuga ya ce daga bisani shugaban ƙasar zai wuce Addis Ababa babban birnin kasar Habasha.

A Habasha Tinubu zai halarci taron shugabannin ƙasashen kungiyar Tarayyar Afirka da za a gudanar daga ranar 12 zuwa 16 ga watan Fabrairu.

A watan Nuwamban shekarar da ta wuce Tinubu ya kai ziyarar aiki ƙasar ta Faransa inda ya gana da shugaban kasa, Emmanuel Macron.

More from this stream

Recomended

Mutane 7 Sun Rasa Rqyukansu, 53 Sun Jikkata Sakamakon Guguwar Iska a Jigawa

Akalla mutane bakwai sun rasa rayukansu, yayin da 53 suka jikkata bayan wata guguwar iska ta yi barna a kananan hukumomi 13 na jihar Jigawa. Rahotanni sun nuna cewa guguwar ta shafi gidaje 5,403 a cikin garuruwa 120, inda ta lalata makarantu sama da 47, asibitoci uku, ofisoshin ‘yan sanda biyu, gidajen zama da sauran […]