
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaba ƙarƙashin jam’iyar, a fadar Aso Rock dake Abuja.
Ganawar ta gudana ne a ofishin shugaban ƙasa dake cikin da fadar ta Aso Rock.
Gwamnonin da aka hanga a wurin taron sun haɗa da Babagana Zulum (Borno), Hope Uzodimma (Imo), Inuwa Yahaya (Gombe), Hyacinth Alia (Benue), Biodun Oyebanji (Ekiti), Peter Mbah (Enugu), da kuma AbdulRahman AbdulRazaq (Kwara).
Wasu daga cikin gwamnonin sun samu wakilcin mataimakansu.
Taron ganawar na zuwa ne kasa da sa’o’i 24 bayan da shugaban ƙasar ya gana da shugabannin majalisar dattawa da aka ce ganawar ta mayar da hankali kan batun sulhu wajen fitar da yan takara.

