Hukumomin Sudan sun ce za su mika tsohon shugaban kasar Omar al-Bashir ga kotun hukunta masu aikata manyan laifuka.
Tsohon shugaban kasar yana fuskantar zarge-zargen kisan kare-dangi, laifukan yaki da kuma na cin zarafin dan adam sakamakon yakin da ya barke a yankin Darfur a 2003.
An hambarar da shi daga kan mulki a watan Afrilun 2019.
Ya zama shugaban kasa ne bayan juyin mulkin da sojoji suka yi a 1989 kuma an zarge shi da yin mulkin kama-karya.