Sojojin Najeriya sun yi mummunar ta’asa wa ƴan bindiga a Kaduna

Dakarun Sojojin Najeriya sun yi nasarar halaka ‘yan bindiga shida da ke addabar mazauna karamar hukumar Birnin-Gwari ta jihar Kaduna.

Mukaddashin daraktan hulda da jama’a na rundunar soji ta daya, Laftanar Kanar Musa Yahaya, ya ce ‘yan bindigar sun haɗu da ajalin nasu ne a ranar Alhamis lokacin da sojojin da ke aiki da sahihan bayanan sirri suka kai wani samame a kauyukansu a Sabon Birnin, Dogon Dawa, Saulwa, Maidaro- Ngede Allah da Kidenda duk a karamar hukumar Birnin-Gwari.

Ya bayyana cewa sojojin sun taɓo ‘yan ta’addan inda nan take suka yi artabu da su har suka kashe shida daga cikinsu.

Sojojin, a cewar kakakin rundunar, sun kuma kwato bindigogin AK-47 guda biyu, da gidan albirushin AK-47 guda hudu, harsashi guda goma sha hudu na 7.62mm, rigunan ‘yan fashi guda arba’in, da kuma babura tara.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]