Sojojin Najeriya Sun Yi Hatsarin Mota A Maiduguri

Sojojin Najeriya tara sun ji raunuka daban-daban bayan da daya daga cikin motocin da suke ciki ta yi hatsari a garin Maiduguri da ke jihar Borno a arewa maso gabashin kasar.

Wata sanarwa da Darektan yada labaran rundunar sojin kasar Birgediya-Janar Onyema Nwachukwu ya fitar a ranar Juma’a ta ce, sojojin suna kan hanyarsu ta kai daukin gaggawa ne a wani yankin garin na Maiduguri a lokacin da hatsarin ya auku.

“Tsantsi ne ya kwashe daya daga cikin motocin sojojin wacce ke dauke da bindiga, hakan ya sa ta zame ta afka gefen hanya, lamarin da ya sa motar ta yi juyin kuli-kulin-kubura.” In ji Nwachukwu.

Lamarin ya auku ne a kusa da garin Kuturu da ke kan hanyar Damaturu zuwa Maiduguri.

“An kai sojojin tara da suka ji rauni wani asibitin soji ana ba su kulawa, amma ba a samu asarar rai ba.”

Babban hafsan sojin kasa Laftanar-Janar Faruk Yahaya ya mika jajensa ga sojojin a cewar sanarwar.

“Janar Yahaya ya yaba da irin kokarin da dakarun suke nunawa wajen kai dauki, yana mai kira a gare su da su zama masu kiyayewa a duk lokacin da za su kai daukin gaggawa.

Dubban dakarun Najeriya na jibge a jihar ta Borno, inda suke yaki da mayakan Boko Haram da ISWAP.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]