Sojojin Najeriya sun kai harin kwanton kan Boko Haram

Jajirtattun sojan Najeriya da suka fito daga Bataliya ta 222 dake Konduga tare da hadin gwiwar wasu manoma sun samu nasarar kai harin kwanton bauna akan yan ta’addar Boko Haram lokacin da suke sintiri akan titin Mushari-Galtimari a jihar Borno.

A wata sanarwa da hedkwatar rundunar sojan Najeriya ta fitar tace yan ta’addar sun je gonakin ne domin satar kayan abinci musamman albasa daga gonakin dake yankin.

Sanarwar ta kara da cewa an kashe dan kungiyar ta Boko Haram daya yayin kai harin ya yin da wasunsu suka tsere.

Yan ta’addar sun bar kekunansu a wurin tare da buhunan albasa da suka sata daga gonakin.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]