Rundunar sojin Najeriya ta tsare wani jami’inta bayan ya harbi wani abokin aikinsa bisa kuskure a wani sansanin soji da ke jihar Borno.
Masanin harkokin tsaro, Zagazola Makama, ya bayyana hakan a wani sako da ya wallafa a shafin X, inda ya ce lamarin ya faru ne a safiyar ranar ashirin ga watan Yuni a wani sansanin tsaro da ke Damboa.
Rahotanni sun ce jami’in, wanda ke aiki da Bataliya ta ashirin da biyar, ya saki bindigarsa bisa kuskure a cikin sansanin, lamarin da ya jikkata wani soja.
An garzaya da sojan da ya samu rauni domin kula da lafiyarsa kafin daga bisani aka kai shi cibiyar jinya ta soji.
Hukumomin soji sun ce sun kwace makamin jami’in tare da tsare shi domin ci gaba da bincike da daukar matakan ladabtarwa idan ya cancanta.
Sojoji Sun Tsare Jami’i Kan Harbin Abokin Aikinsa Bisa Kuskure A Borno

