Sojoji sun kashe ‘yan bindiga 100 tare da kwato makamai a Zamfara da Katsina – AREWA News

Rundunar sojojin Nijeriya sashin ‘Operation Hadarin Daji,’ sun yi nasarar kashe ‘yan bindigar da suka ki mikawa wuya 100 tare da manyan kwamandojin ‘yan bindigar 6 a jihohin Katsina da Zamfara.

Jami’in watsa labarai na rundunar sojojin Kaftin Ayobami Oni-Orisan, ne ya sanar da hakan.

Ayobami, ya ce rashin mikawa wuya ga gwamnatin jihar Zamfara da ta bullo da shi yasa dakarun suka yi farautar ‘yan bindigar, hakan yasa suka yi nasara kashe su.

Ya kara da cewa, daga ranar 16 ga Disamba 2019 zuwa 9 ga Janairu 2020, dakarun sojojin Najeriya tare da takwarorin su na sama da na ruwa da rundunar ‘yan sandan Najeriya da jami’an tsaron farin kaya DSS da sauran jami’an tsaro sun gudanar da farmaki ga ‘yan bindigar don tabbatar da zaman lafiya a yankunan jihohin.

More News

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...

Delta: An dawo da gawarwakin sojojin da aka kashe Abuja don yi musu jana’iza

Gawarwakin sojojin da aka kashe a jihar Delta kwanan nan sun isa maƙabartar sojoji ta kasa da ke Abuja. Gawarwakin sun iso ne da misalin...