Sojoji Sun kashe Mayaƙan Boko Haram 3 Tare Da Ceto Mutane 9

Dakarun sojan Najeriya na rundunar, Operation Haɗin Kai sun kashe mayaƙan Boko Haram uku a ƙaramar hukumar Bama dake jihar Borno.

A cewar Zagazola Makama wani masani dake wallafa bayanai kan sha’anin tsaro a yankin tafkin Chadi ya ce an kashe mayaƙan ne lokacin da sojoji suke gudanar da aikin sintiri.

Ya ce an kashe ƴan ta’addar ne a ƙauyen Churchur a yayin musayar wuta lokacin da sojojin suke sintiri.

A wani farmakin na daban sojojin sun samu nasarar ceto mutane 9 da suka haɗa da mata uku da ƙananan 6 s sun kuma lalata sansanin mayaƙan na Boko Haram bayan da suka tsere.

Hakan na zuwa ne ƴan kwanaki bayan da sojoji suka kashe wasu mutane uku a wani samame da suka kai maɓoyar Boko Haram da kuma mayaƙan ISWAP a jihohin Borno da Katsina

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...