Sojoji Sun Kashe Gawurtaccen Ɗan Bindiga Boderi

Dakarun rundunar sojan Najeriya sun kashe wasu gawurtattun masu garkuwa da mutane da suka jima suna addabar al’umma.

Mai magana da yawun rundunar sojan Najeriya, Onyeama Nwachukwu shi ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis .

Ya ce ƴan fashin daji shida aka kashe a yayin farmakin da aka kai a yankin Bada-Riyawa dake kan hanyar Birnin Gwari zuwa Kaduna a ranar 22 ga watan Faburairu.

Ya ce bayanan sirri sun bayyana cewa Boderi da Bodejo  gawurtattun masu garkuwa da mutane na daga cikin yan fashin dajin da aka kashe a yayin arangamar.

Mutanen biyu sune ke da alhakin kai hari kan makarantar sojoji ta NDA,  kwalejin aikin gona dake Afaka, jami’ar Greenfield da kuma makarantar ƴan mata ta Yauri.

Baderi ya shafe shekaru da dama yana addabar al’umma kana ana zarginsa da haɗa baki da ƴan ta’adda domin kafa masu sansani a dazukan dake yankunan da yake da iko da su.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani ɓangare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...