Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga Biyu Tare Da Ceto Mutane 20 Da Aka Yi Garkuwa Dasu A Jihar Zamfara

Dakarun Rundunar Sojan Najeriya sun kashe ƴan fashin daji biyu ciki har da wani gawurtaccen ɗan bindiga a jihar Zamfara.

A wata sanarwa ranar Talata, Yahaya Ibrahim jami’in yaɗa labarai na rundunar Operation Hadarin Daji ya ce an kashe ƴan ta’addar ne a wani farmaki da aka kai maɓoyarsu dake kananan hukumomin Zurmi da Birnin Magaji a jihar Zamfara.

Ibrahim ya ce sojojin sun ceto mutane 20 da aka yi garkuwa da su da suka haɗa da mata da kuma ƙananan yara.

Ya ce sojojin sun samu nasarar lalata maɓoyar yan ta’addar da kuma maɓoyar wani fitaccen ɗan bindiga da ake kira Sule.

More News

Tayoyin jirgin saman Max Air sun fashe a Yola

Jirgin saman kamfanin Max Air ƙirar Boeing 737 mai rijistar namba 5N-ADB dake ɗauke da fasinjoji 118 da ma'aikata 6 ya gamu da matsala...

Ɗan majalisar wakilai ta tarayya ya mutu

Hon. Olaide Akinremi Jagaba mamba a majalisar wakilai ta Najeriya dake wakiltar mazaɓar Ibadan North a majalisar ya mutu. Kawo yanzu babu cikakken bayani kan...

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...