Sojoji Sun Kama ‘Yar Chadi Da Ake Zargin Tana Kai Wa ‘Yan Ta’adda Kayan Maye A Borno



Dakarun Operation HADIN KAI sun kama wata ‘yar ƙasar Chadi mai suna Rachael Samuel, mai shekaru 48, da ake zargin tana kai wa ƙungiyoyin ta’addanci da ke yankin Tafkin Chadi kayan maye da giya.

Mai riƙon mukamin Jami’in Yaɗa Labarai na rundunar, Kyaftin Mohammed Goni, ya ce an kama matar ne a kan hanyar Maiduguri–Monguno bayan samun sahihan bayanan sirri.

Ya ce an ƙwato tabar wiwi mai nauyin kusan kilogram 30, kwantenoni biyu na wani sinadari da aka fi sani da “Suck and Die”, kwalaben giya, wayar salula, katunan ATM biyu, kuɗi da sauran kayayyaki.

Rundunar ta ce matar na tsare, yayin da za a miƙa kayayyakin da aka ƙwato ga hukumomin da suka dace domin ci gaba da bincike da kuma yiwuwar gurfanar da ita a gaban kotu. Ta kuma bayyana cewa samamen na daga cikin ƙoƙarin da ake yi na katse hanyoyin samar da kayan tallafi ga ƙungiyoyin ta’addanci a Arewa maso Gabas.

More from this stream

Recomended

Mutane 7 Sun Rasa Rqyukansu, 53 Sun Jikkata Sakamakon Guguwar Iska a Jigawa

Akalla mutane bakwai sun rasa rayukansu, yayin da 53 suka jikkata bayan wata guguwar iska ta yi barna a kananan hukumomi 13 na jihar Jigawa. Rahotanni sun nuna cewa guguwar ta shafi gidaje 5,403 a cikin garuruwa 120, inda ta lalata makarantu sama da 47, asibitoci uku, ofisoshin ‘yan sanda biyu, gidajen zama da sauran […]