Sojin Saman Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Bindiga Kusan 100 a Jihar Zamfara

VOA Hausa

Daraktan watsa labarai na rundunar sojin saman Najeriya Air Commodore Ibikunle Daramola, ya bayyana cewa an kai farmakin ne domin sa kafar wando daya da ‘yan tada kayar baya, da wargaza sansanoninsu domin samar da zaman lafiya a yankin.
Daramola ya ce an kai farmakin mai take ‘OPERATION WUTAR DAJI 2’ da ke karkashin ‘Operation Hadarin Daji’, a dazukan Damborou, Kwuyambana, Dutsen Asolavda kuma Duten Bagai.
Babban Hafsan Sojin Saman Najeriya, Air Marshall Sadique Abubakar wanda yanzu haka yake yankin, ya ce suna samun nasarori a farmakin da suke kai wa kan sansanonin ‘yan bindigar a jihar ta Zamfara.

Hafsan Sojin Saman Najeriya Sadique Abubakar tare da Shugaba Muhammadu Buhari
Hafsan Sojin Saman Najeriya Sadique Abubakar tare da Shugaba Muhammadu Buhari

Abubakar ya ce suna amfani da na’urori da ke gano dukkan maboyar ‘yan ta da kayar bayan, wanda hakan ya ba su damar wargaza su.
Gwamnatin Jihar zamfara ta bakin kakakin gwamnan jihar Zailani Baffa, ta bayyana gamsuwa da yadda sojojin suke ci gaba da aikin fatattakar ‘yan bindigar da suka hana jama’a walwala a jihar.

More News

Tayoyin jirgin saman Max Air sun fashe a Yola

Jirgin saman kamfanin Max Air ƙirar Boeing 737 mai rijistar namba 5N-ADB dake ɗauke da fasinjoji 118 da ma'aikata 6 ya gamu da matsala...

ÆŠan majalisar wakilai ta tarayya ya mutu

Hon. Olaide Akinremi Jagaba mamba a majalisar wakilai ta Najeriya dake wakiltar mazaɓar Ibadan North a majalisar ya mutu. Kawo yanzu babu cikakken bayani kan...

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...