Shettima ya dawo Najeriya bayan ziyarar aiki kasashen Guinea da Switzerland

Sulaiman SaadHausa6 months ago

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya dawo gida birnin tarayya Abuja bayan ya shafe kusan mako guda a kasashen Guinea Conarkry da kuma Switzerland.

Shettima ya sauka a filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe dake Abuja da ya wakilci shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu a wurin bikin rantsar da, Mamadi Doumbouya shugaban kasar Guinea da kuma jagorantar tawagar Najeriya a a wurin taron tattalin arziki na duniya da aka yi birnin Davos na kasar Switzerland da aka saba gudanarwa a kowace shekara.

Bayan saukarsa a Najeriya Shettima ya bayyana cewa Najeriya ta sake kwato matsayinta na kujerar kan gaba a tattaunawa da suka shafi tsare-tsare a matakin yankin nahiya

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...