Saudiyya za ta daina aiwatar da hukuncin kisa kan kananan yara

Women protest outside the Saudi consulate in New York on 1 June 2019 to protest against the trials of three clerics in Saudi Arabia

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Amnesty ta ce Saudiyya ta yanke hukuncin kisa kan mutum 184 a 2019

Saudiyya ta sanar da cewa daga yanzu ta daina yanke hukuncin kisa kan wadanda suka aikata laifuka yayin suna yara kanana.

Hukumar da ke kula da hakkin dan Adam ta kasar ce ta bayyana haka.

Sarki Salman ya sanya hannu kan dokar tabbatar da sanarwar wadda ta zo kwana biyu bayan da Sarkin ya hana yi wa masu laifi bulala a kasar.

Hukumar kula da hakkin yara kanana ta Majalisar Dinkin Duniya – wadda kasar Saudiyya mamba ce ta hukumar ta ce irin wannan hukunci bai kamata a rika yanke shi kan kananan yara ba.

Masu fafutukar kare hakkin bil Adama na cewa Saudiyya na cikin jerin kasashe masu gallaza wa al’ummarsu a duniya.

Sun ce ana matukar hana mutane fadan albarkacin bakinsu musamman a fagen sukar gwamnati, domin anan iya kama su babu shari’a.

Saudiyya ta yanke hukuncin kisa kan mutum 184 a 2019, inji Amnesty International. A cikinsu akwai wani mutum da aka yanke wa hukuncin kisa kan laifin da ya aikata a lokacin yana yaro.

Hukumomin Sauddiyya ba su sanar da ranar da dokar za ta fara aiki ba.

More News

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...

An fara rushe wasu gine-gine 500 a kasuwar Karmo dake Abuja

Hukumar FCTA dake kula da birnin tarayya Abuja ta fara rushe gine-gine sama da 500 da aka yi ba bisa ka'ida ba a kasuwar...

Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa

A ranar Alhamis ne shugaba Bola Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa, a ziyarar da Faye ya...

NEMA ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo dasu gida daga ƙasar Chad

Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Ƙasa NEMA ta ce ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo da su bayan da su ka maƙale...