Sarki Salman na Saudiyya ya kori ‘yan gidan sarautar daga muƙamansu

Crown Prince Mohammed bin Salman

Bayanan hoto,
Ana yi wa Yarima Mai Jiran Gado Mohammed bin Salman kallon shugaban Saudiyya

An kori jami’an kasar Saudiyya da dama, ciki har da iyalan gidan sarauta guda biyu.

Wata sanarwa ta bayyana cewa Sarki Salman ya sauke Yarima Fahad bin Turki daga kan mukaminsa na kwamandan hadakar dakarun tsaron kasar da ke jagorantar yakin da ake yi a Yemen.

Kazalika an sauke dansa, Abdulaziz bin Fahad, daga mukamin mataimakin gwamna.

Mutanen biyu, tare da karin mutum hudu, suna fuskantar bincike bisa “zargin wadaƙa da kudi” a Ma’aikatar Tsaron kasar.

Yarima Mai Jiran Gadon Sarautar Saudiyya Mohammed bin Salman, wanda shi ne dan sarkin kuma ake yi masa kallo a matsayin mutumin da zai gaji Sarki Salman, yana jagorantar yaki da cin hanci da ake zargin ana aikatawa a gwamnati.

Sai dai masu suka na cewa yana yin hakan ne da zummar kawar da mutanen da ka iya yi masa zagon-kasa a yunkurinsa na zama sarki.

A farkon wannan shekarar, mujallar Wall Street Journal ta ruwaito cewa an kama manyan shugabannin gidan sarautar kasar guda uku, cikinsu har da kanin sarkin, Yarima Ahmed bin Abdulaziz da kuma tsohon Yarima mai jiran gado Mohammed bin Nayef.

Babban abin da ya ja hankalin duniya kan yaki da cin hanci a Saudiyya shi ne kamen da aka yi wa wasu fitattun ‘yan gidan sarautar kasar, ciki har da ministoci da ‘yan kasuwa, inda aka tsare su a shahararren otal din nan na Ritz-Carlton da ke Riyadh a 2017.

An saki galibinsu daga bisani, kodayake sai da suka bayar da dala biliyan 106.7.

Yarima Mai Jiran Gado Mohammed bin Salman mai shekara 35, ya sha yabo daga kasashen duniya a 2016 lokacin da ya yi alkawarin kawo sauye-sauye a fannin tattalin arziki da zamantakewa a kasar da ke da wuyar sha’ani.

Sai dai ya rika shan suka kan batutuwa da dama, ciki har da kisan dan jaridar Saudiyya Jamal Khashoggi a ofishin jakadancin kasar da ke Istanbul na Turkiyya.

More News

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...