Samuel Ortom: Buhari ya ce yana takaici kan zarge-zargen da Gwamnan Benue yake yi masa

Ortom

Asalin hoton, Getty Images

Shugaban Najeirya Muhammadu Buhari ya ce abin takaici ne irin yadda gwamnan jihar Benue Samuel Ortom yake zarginsa da aikata wasu laifuka.

Shugaba Buhari ya bayyana haka ne a wata sanarwa da mai magana da ywunsa Malam Garba Shehu ya aike wa manema labarai ranar Juma’a da safe.

Ya mika jajensa ga al’ummar jihar ta Benue wadanda suka rasa rayukansu sakamakon hare-haren da aka kai musu a baya bayan nan.

Rahotanni sun ambato Gwamna Ortom yana zargin Shugaba Buhari da mara wa makiyaya baya a kashe-kashen da yake cewa sun yi a jihar ta Benue.

Sai dai shugaban kasa ya kara da cewa babu kamshin gaskiya a zarge-zargen yana mai cewa “babu wata gwamnatin da take da hankali da za ta ji dadin irin wadannan kashe-kashe na sojoji da mutanen da ba su ji ba ba su gani ba da ke zaune a sansanonn ‘yan gudun hijira.”

Shugaba Buhari “ya bayyana takaicinsa da bakin cikin jin Samuel Ortom, gwamnan jihar Benue yana yin jerin zarge-zarge a kansa da gwamnatinsa sakamakon hare-haren da aka kai a jhar a kwanakin baya,” in ji Malam Garba Shehu.

Shugaban kasar ya bukaci hadin gwiwa a matakai daban-daban domin shawo kan kashe-kashe da kuma rikice-rikicen da ake yi a kasar.

“Shugaba Buhari yana matukar jin zafin rikice-rikicen da ake yi ba wai kawai a jihar Benue har ma sauran sassan kasar kuma yana tsammanin jami’an tsaro za su shiga kowanne lungu da sako na kasar domin kama wadanda suke aikata wadannan laifuka da kuma gurfanar da su a gaban kuliya,” in ji Malam Garba Shehu.

Ya yi kira ga gwamnan jihar ya bai wa gwamnatin tarayya hadin kai domin shawo kan matsalolin tsaro da ke addabar jihar.

(BBC Hausa)

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...