Premier League: Chelsea ta zazzaga wa Everton kwallaye | BBC Hausa

Chelsea

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Olivier Giroud ne ya cike wa Chelsea kwallo ta hudu da ta ci

Chelsea ta yi wa Everton ruwan kwallaye kuma tana ci gaba da rike matsayinta na hudu a teburin Premier.

Chelsea ta fara zira kwallo ta farko ne ta hannun matashin dan wasanta Mason Mount a minti na 14 da fara wasan.

A minti na 21 ne dan wasan gaban Sifaaniya Pedro ya zira kwallo ta biyu, wanda hakan ya kara bai wa Chelsea kwarin gwiwa.

Bayan an dawo daga hutun rabin lokaci dan wasan gefe na Chelsea dan Brazil, Willian ya kara ta uku a minti na 51.

Minti uku tsakani dan wasan gaban Faransa Olivier Giroud ya kara ta hudu.

Cikin wasa 24 da Everton ta buga a Stamford Bridge a Premier ba ta yi nasara ko daya ba – ta yi canjaras 11 ta yi rashin nasara 13.

Tun daga washegarin ranar Kirsimati da Carlo Ancelotti ya karbi Everton ya fi kowanne kulob samun maki, inda ya samu 18 – Liverpool da ta hada 30 da Manchester City mai 19 ne kawai suka fi shi.

Yanzu dai Chelsea za ta ziyarci Aston Villa a ranar Asabar mai zuwa, yayin da Everton za ta buga wasan hamayya da Liverpool.

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa É—aya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faÉ—a tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...