Namadi Sambo zai jagoranci kwamitin sake gina masallacin Juma’a na Zaria da ya ruguje

Sarkin Zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli ya kafa wani kwamitin kwararru mai mambobi 11 kan sake gina babban masallacin Juma’a na Zaria da ya rushe.

A wata sanarwa da Abdullahi Aliyu Kwarbai mai magana da yawun masarautar ya ce tsohon mataimakin shugaban kasa kuma Sardaunan Zazzau, Arc Namadi Sambo shi ne zai kasance shugaban kwamitin a yayin da Arch. Ibrahim Waziri zai zamo sakataren kwamitin.

Sanarwar ta kara da cewa “mambobin kwamitin sun haɗa da Arch. Abubakar Abdulkadir, Professor Kabir Bala, Vice Chancellor, ABU, Arch. Muhammadu Aminu Idris, Sheikh Dr. Hayatuddeen, Arch. Gambo Hamza da TPL Bello Nuhu Yakubu.

“Sauran su ne Bld. Lawal Magaji, Arch. Isa A. A and Arch. Haruna Abubakar Bamalli.”

Idan za a iya tunawa a ranar Juma’a 11 ga watan Agusta na shekerar 2023 wani sashe babban masallacin Juma’a na masarautar Zazzau ya ruguzo kan masallata.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]