‘Naira tiriliyan daya ta salwanta a Bauchi karkashin Yuguda da M.A.’

Bauchi Governor Bala Muhammad

Hakkin mallakar hoto
Bauchi State Government

Image caption

Gwamnan Bauchi Bala Kaura

—BBC Hausa

Kwamitin da gwamnatin jihar Bauchi da ke Najeriya ta kafa domin bin diddigi da karbo kadarorin gwamnati da ake zargin an wawure, ya yi zargin cewa an salwantar da kudi fiye da naira tiriliyan daya.

Kwamitin ya ce a zamanin tsofofin gwamnonin jihar biyu wato Malam Isa Yuguda da kuma Barista Muhammad Abdullahi Abubakar kudaden suka salwanta.

Mutanen biyu sun yi mulki a lokuta daban-daban daga 2007 zuwa 2019.

Kwamitin ya ce ko da ya ke ya yi nasarar karbo motoci masu yawan gaske da wasu kadarori, to amma har yanzu ya kasa bambaro fiye da naira tiriliyan daya daga gwamnatocin biyu da suka shude.

Tsofofin gwamnoni biyu, Isa Yuguda da Muhammad Abdullahi Abubakar ne suka jagoranci gwamnatin jihar daga 2007 zuwa 2019.

Don haka kwamitin ke bukatar tsoffin jami’an gwamnatin su maido kudaden da ake zargin sun wawure.

Malam Musa Azare shi ne mataimakin kakakin kwamitin, ya yi bayani kan abin ta’ajibi da suka bankado yayin aikinsu na watanni takwas.

“Akwai abubuwa da dama da muka gano daga kwangiloli da aka bayar da su.”

Ya kara da cewa: “Ko dai an bayar da su amma ba a yi ba bayan an fitar da kudadensu, ko kuma an yi su rabi-da-rabi. Ko ma an bayar da su kan kudaden da ake zargin sun yi yawa.”

Ya ce sun kira ‘yan kwangilan da suka aiwatar da wadannan ayyukan domin su gano ainihin gaskiyar lamarin.

“Wasunsu sun amsa kiran kuma sakamakon bayanan da suka bayar ne ma aka saka cikin wannan rahoton binciken,” inji shi.

Cikin wadanda kwamintin ya kra har da wasu jami’an gwamnatocin da suka gabaci wannan.

Martanin tsofaffin gwamnatocin

Gwamnatocin biyu da duka shude a jihar Bauchi sun fito suna musanta zargin wawure sama da naira tiriliyan dayan da wannan kwamitin binciken yayi mu su.

Alhaji Salisu Ahmad Barau Tafawa Balewa, shi ne mai magana da yawun tsohuwar gwamnatin jihar ta Malam Isa Yuguda, wanda ya yi gwamna daga 2007 zuwa 2015.

Ya ce “In mai fadan magana wawa ne, ai mai jinta ba wawa ba ne. Gwamantin Isa Yuguda karkashin jam’iyyar PDP a wancan zamanin ta sami jimillar kusan Naira biliyan 600 ne.”

Ya kara da cewa cikin biliyan dari shidan, gwamantinsu ta kashe kimanin biliyan 500 ne wajen biyan albashin ma’aikata da sauran ayyuka na yau da kullum.

“Saura kuma ne Isa Yuguda yayi tsimi da dabara har ya yi katafarun ayyuka a jihar Bauchi kamar filin jirgin sama da jami’ar jihar, da kuma asibitin kwararru da sauran su.”

Shi ma tsohon gwamnan jihar Barista Abdullahi Abubakar da ya mulki jihar daga 2015 zuwa 2019, cewa ya ke yi bita-da-kullin siyasa kawai gwamnatin Bala Kaura ke yi masu.

Malam Ali M Ali shi ne mai magana da yawun tsohon gwamna M. Abubakar.

Kakakin na tsohon gwamna ya kuma ce batun da masu mulkin jihar na yanzu ke yi, wata dabara ce ta kawar da hankali daga zarge-zargen rashawa kan jami’an gwamnatin yanzu.

“Gaba daya kudaden da aka samu a shekara biyar ba su kai biliyan 350 ba. Alkaluman suna nan. Ina aka samo batun tiriliyan? Hankali ba zai dauka ba.”

Ya kuma zargi gwamnati mai ci ta Bala Muhammad, Kauran Bauchi da “gaza aiwatar da wani abin a zo a gani cikin watannin da suka sami kansu a mulkin jihar.”

To amma kwamitin ganowa da sake karbo dukiyar gwamnatin na musanta zargin bita-da-kulli da kuma kokarin badda-bami.

Gwamnatoci biyu da suka gabata a jihar ta Bauchi – wadanda kwamitin ke zargi da karkatar da dukiyar jihar da ta kai sama da naira tiriliyan daya – su ma sun gudanar da irin wannan binciken a baya.

Su ma sun rika zargin gwamanatocin da suka gabace su da yin ruf da ciki da dukiyar talakawa, amma daga bisani sai aka ji shiru kan lamarin.

More News

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...