Hadarin mota a Kano ya yi sanadin mutuwar mutane akalla 18, lamarin da ya jawo hawaye a idanun masoya da ‘yan uwa.
Rahotanni sun bayyana cewa, wannan mummunan lamari ya faru ne a kan hanyar Kano zuwa Ringim a karamar hukumar Gabasawa a jihar.
Kwamandan hukumar kiyaye haddura ta kasa (FRSC) Ibrahim Abdullahi ya tabbatar wa manema labarai afkuwar hatsarin.
Ya bayyana cewa, hatsarin ya rutsa da fasinjoji 35 a cikin motocin bas guda biyu, daga cikinsu 18 sun kone kurmus, yayin da wasu 12 suka samu munanan raunuka.