Motar da Adam Zango ya ce ya saya milyan 23 ba tasa ba ce, tawa ce na ba shi shan miya – Z-Preety

Fitacciyar jarumar finafinan Hausa, Zulaihat Ibrahim, wacce aka fi sani da Zpreety, ta yi wata muhimmiyar magana akan motar da Adam Zango yace ya saya naira miliyan 23.

Zulaihat wacce aka fi sani da Zpreety ta bayyana cewa wannan magana ba haka take ba, inda ta ce mota dai tata ce ta ara masa. Ta kara da cewa ta yi hakan ne domin ta nunawa duniya yadda take girmama Adam Zango, amma kuma sai ya ɓuge da yi wa mutane karya.

Zulaihat ta bayyana cewa motar nan da Adam Zango ya dinga sanyawa a kafafen sada zumunta ba tashi bace motarta ce.

Ta bayyana hakan ne a cikin wani bidiyo da ya dinga yawo a kafafen sada zumunta, inda aka nuno ta a tsaye kusa da motar tana magana.

Zulaihat din ta ce “Mutane na taa tambaya ta cewa dana sami kudin wakar babban yaro mai na yi da shi, gaskiya ce nake so na fada yau, motar nan da kuka gani Baba Adamu yana hawa tsakani da Allah tawa ce.

“Da aka bani ita don nake hawa, sai na ga cewa yana da kyau ka girmama na gaba gare ka, sai na dauka na ba shi akan zai hau na tsawon wata biyar daga nan zan karba na cigaba da amfani da motata.”

A jikin bidiyon Zulaihat ta nuna asalin motar Adam Zango, domin ta kara tabbatarwa da mutane cewa motarta ce.

“Ina dai so na nunawa duniya ta san ainahin abinda ke faruwa ne saboda kowa ya san cewa karya babu kyau.” Makonnin da suka gabata ne dai hotunan jarumi Adam Zango akan wata jar mota suka dinga yawo a shafukan sada zumunta, inda aka bayyana cewa ya sayi motar naira miliyan 23.

More News

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon ɗaya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Gidaje 8925

Gwamnatin tarayya ta ce ta fara raba gidaje 8925  ga mutanen da suka nema kuma suka cancanci a basu a faɗin ƙasa baki ɗaya...

Ƴan Bindiga A Zamfara Sun Kashe Sakataren Jam’iyar PDP

Wasu ƴan bindiga da ba a san ko suwaye ba sun kashe, Musa Ille  sakataren jam'iyar PDP na ƙaramar hukumar Tsafe a jihar Zamfara. Zagazola...